• Ba A Yi Ma Nnamdi Kanu Adalci Ba- Emmanuel Kanu
    Nov 21 2025

    Send us a text

    Hukuncin da kotun tarayya ta Abuja ta yanke wa shugaban haramtacciyar ƙungiyar IPOB, Mazi Nnamdi Kanu, ya sake tayar da kura a tsakanin magoya bayansa, ‘yan yankin Kudu maso Gabas, da al’ummar Najeriya gaba ɗaya.


    Yayin da gwamnati ke cewa hukuncin ya biyo bayan dogon shari’a da hujjoji da suka tabbatar da aikata laifukan da ake tuhumarsa da su, wasu na ganin batun na da matuƙar sarkakiya musamman ma yadda iyalansa da magoya bayansa ke kallon wannan hukunci.


    Shin ko yaya ‘yan uwan Nnamdi Kanu suka kalli wannan hukunci?

    Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

    Show More Show Less
    25 mins
  • Halin Kunci Da Matan Da Aka Yi Garkuwa Da Su Ke Tsintar Kansu A Ciki
    Nov 20 2025

    Send us a text

    Mata da dama da aka yi garkuwa da su na shiga wani irin mawuyacin hali yayin da suke hannun wadanda suka sace su, suna fuskantar rayuwar kaskanci, da cin zarafi, da muzgunawa da wasu irin yanayi wanda sai ka tausaya musu.


    Irin wadannan mata a wasu lokutan basa tsira da rayukansu, a wasu lokutan kuma ko sun tsira, sukan shiga halin ciwon damuwa wanda ke daidaita musu rayuwa, a wasu lokutan ma har sai sun ji kamar su dauki rayuwar su.


    Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba ne kan irin halin da irin wadannan mata ke shiga da kuma hanyoyin da zasu bi don dawo da martaba a rayuwarsu.

    Show More Show Less
    19 mins
  • Matsayar Doka Kan Taron Da Jam'iyyar PDP Ta Gudanar
    Nov 17 2025

    Send us a text

    Matsayar doka ta zama babbar abun tattaunawa a Najeriya yayin da jam’iyyar PDP ta gudanar da taron ta na kasa duk da mabanbantan hukunce hukunce daga kotuna biyu.


    Umarnin kotu guda yana goyon bayan taron, ɗayan kuwa ya haramta shi gaba ɗaya. Wadannan hukunce hukunce ba baiwa jam’iyyar damar yi ko haramta musu taron kadai suka yi ba, harda baiwa hukumar zabe ta kasa umurnin saka ido ko haramta musu wannan dama yayin taron.

    Duk da wadannan hukunce hukunce, jam’iyyar ta gudanar da taron inda ta zabi shugabannin da zasu cigaba da jan ragamar al’amuranta da kuma daukar wasu kwararan matakai.


    Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

    Show More Show Less
    25 mins
  • Dalilan Da Ke Hana Manoman Najeriya Noman Rani
    Nov 14 2025

    Send us a text

    A duk shekara bayan girbin damina, ana sa ran manoma su ci gaba da noma a lokacin rani domin tabbatar da wadatar abinci da bunkasar tattalin arziki. Sai dai hakan na fuskantar kalubale da dama da ke hana yawancin manoma shiga noman rani.


    Kamar yadda masana suka sha bayyanawa, akwai dalilai da dama dake hana manoma shiga noman rani a duk lokacin da aka ce damina ta tattara inata intat.

    Shin ko wadanne kalubale ne ke hana manoma shiga noman rani bayan damuna ta wuce?


    Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

    Show More Show Less
    27 mins
  • Yadda Raguwar Maniyyatan Najeriya Ke Tasiri Ga Aikin Hajji A Najeriya
    Nov 13 2025

    Send us a text

    A kwanakin nan ana samun raguwar kujerun maniyyata aikin Hajji daga Najeriya, abin da ya jawo fargaba ga masu shirin zuwa kasa mai tsarki da kuma masu hidimar su.


    A da, Najeriya na samun kujeru sama da dubu casa’in daga gwamnatin Saudiyya, amma cikin shekaru kadan da suka gabata adadin ya ragu zuwa kusan dubu sittin da biyar.

    Kazalika a yanzu gwamnatin na saudiyya ta bayyana cewa idan har maniyyatan Najeriya basu biya cikakken kudaden hajjin bana ba kafin wa'adin da suka gindaya, to akwai alamun sake rage yawan kujerun zuwa dubu hamsin.


    Ko yaya kara raguwar kujerun maniyyatan Najeriya ke kara tasiri ga Najeriya?

    Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokacin zai yi duba a kai.

    Show More Show Less
    27 mins
  • Dalilan Malaman Jami’oi Masu Zaman Kansu Na Shiga Kungiyar ASUU
    Nov 11 2025

    Send us a text

    A yayin da tattaunawa kan makomar ƙungiyar malaman jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ke ci gaba da ɗaukar hankali, batun yadda za a haɗa jami’o’i masu zaman kansu cikin tsarin ƙungiyar ya sake tasowa.


    Wasu na ganin wannan sabon yunƙuri zai iya zama sabuwar hanyar ƙarfafa hadin kai tsakanin malamai, yayin da wasu ke gargadin cewa hakan na iya kawo tsaiko ga karatun wasu dalibai dake kauracewa jami’oin gwamnati sakamakon yawan yajin aiki da suke tsunduma lokaci zuwa lokaci.


    Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.

    Show More Show Less
    25 mins
  • Dalilan Yaduwar Cutuka A Irin Wannan Lokaci
    Nov 10 2025

    Send us a text

    Da zarar damuna ta fara bankawana, yanayi na sanyi da zafi kan fara sallama, wanda hakan kan zo da rashin lafiya dake yaduwa a cikin alumma.


    Ko wadanne dalilai ne suka sa ake samun yaduwar rashin lafiya a wannan lokaci?


    Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.

    Show More Show Less
    28 mins
  • Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Cutar Basir
    Nov 6 2025

    Send us a text

    Cutar basir na daga cikin cututtukan da mutane da dama ke da mabanbantan ra’ayoyi akan ta.

    A lokuta da dama za ka ji yadda mutane ke fadin dalilai daban daban da ke janyo cutar basir, yayin da wasu ke ganin yawan zama ne ke kawo ta, wasu kuwa gani suke yi zaki da maiko ne ke kawo ta.

    Wannan shine abun da da yawa daga cikin mutane suka sani kan wannan cuta, sai dai masana kiwon lafiya na da nasu fahimtar daban kan wannan cuta.

    Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai tattauna ne kan cutar basir da hanyoyin magance ta.

    Show More Show Less
    26 mins