• Abin Da Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Sa Cin Kifi Yadda Ya Kamata
    Jul 10 2025

    Send us a text

    Duk da amfanin kifi ga lafiyar jikin mutum da kuma samar da kudin shiga masana sun ce ba a amfani da shi yadda ya kamata a Najeriya.


    Baya ga bai wa jiki lafiya, kifi ka iya samar da kudaden shiga ga daidaikun ’yan Najeriya da ma kasar gaba daya.


    Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan dalilan da suka sa ’yan Najeriya basa samun cin kifi kamar yadda ya kamata.

    Show More Show Less
    28 mins
  • Sarkakiyar Dake Gaban Hadakar ADC -- Atiku Ko Peter Obi
    Jul 8 2025

    Send us a text

    'Yan Najeriya suna ci gaba da tafka muhawara a kan wanda jamiyyar hadaka ta ADC zata tsayar takarar Shugaban Kasa a zaben 2027.


    Yayin da wasu suke ganin Atiku Abubakar yana da dimbin magoya baya, wasu kuwa gani suke yi shi ma Peter Obi ba kanwar lasa bane.

    Ko me zai faru idan daya daga cikin su ya samu tikitin tsayawa takara a 2027?


    Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan wannan lamari.

    Show More Show Less
    27 mins
  • Mene Ne Tasirin Nadin Mataimaka Na Musamman A Rayuwar Jama’a?
    Jul 7 2025

    Send us a text

    Wadanda aka zaba su rike mukaman gwamnati kan nada wasu mukarrabai don su taya su sauke nauyin da aka dora musu.


    Wasu na zargin nadin baya rasa nasaba da sakayya ga irin rawar ga wadanda aka nada saboda rawar da suka taka yayin yakin neman zabe.

    Ko irin wadannan nade-nade na da wani tasiri ga rayuwar alumma?


    Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan nade-naden masu taimakawa shugabanni da irin tasirin da suke dashi.

    Show More Show Less
    26 mins
  • Shin Ko Hadakar Sabuwar Jamiyyar ADC Za Ta Fidda Wa ‘Yan Najeriya Kitse Daga Wuta?
    Jul 4 2025

    Send us a text

    Yan Najeriya da dama na ta bayyana mabanbantan ra’ayoyi kan sabon hadakar ‘yan siyasa zuwa sabuwar jami’yyar ADC.


    A yayin da wasu ke ganin wannan hadaka za ta cire musu kitse daga wuta, wasu kuwa gani suke yi duk kanwar ja ce.

    A ranar laraban nan ne dai gaggan ‘yan siyasa daga jamiyyu daban daban suka hadu don dinkewa wuri daya da niyyar kalubalantar jamiyya mai mulki ta APC, a cewar su za su ceto Najeriya daga halin da jamiyyar ta jefa su a ciki.


    Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan ko sabuwar hadakar jamiyyar ADC za ta fidda ‘yan Najeriya daga matsalar da suka ce suna ciki?

    Show More Show Less
    27 mins
  • Boyayyun Kalubalen Da Sabuwar Hadakar ADC Za Ta Iya Fuskanta
    Jul 3 2025

    Send us a text

    Tun kafin sanar da sabuwar kawance da suka hada da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar da Peter Obi da Nasir El’rufai da wasu manyan ‘yan siyasa ne aka fara zargin yiwa wannan hadaka zagon kasa da kawo cikas ga tafiyar wannan hadaka.


    Daya daga cikin irin wadannan zagon kasa da ake zargin wasu da yiwa wannan sabuwar hadaka itace na sanar dasu rashin samun dakin taron da suka shirya gudanar da taron lokaci kalilan gabanin taron.


    Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan boyayyun kalubalen da sabon hadakar jamiyyar ADC zata iya fuskanta gabanin 2027.

    Show More Show Less
    28 mins
  • Halin Da Alummar Mokwa Ke Ciki Wata Guda Bayan Ambaliya
    Jul 1 2025

    Send us a text

    Tun bayan da ambaliyan ruwa ya ci wasu sassan garin Mokwa ne dai alummar garin suka fada halin neman taimako.

    A yayin da gwamnatin tarayya da ma wasu daidakun mutane suka taimaka ma wadanda abun ya shafa da kudi da ma wasu kayayyakin masarufi, wasu daga cikin alummar sun bayyana rashin jin dadin su ga yadda alamura ke gudana a garin Mokwa.

    Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai nazari ne kan halin da alummar Mokwa ke ciki wata guda bayan ambaliyar ruwan da ci wasu sassan na garin.

    Show More Show Less
    25 mins
  • Yadda Za A Kawo Karshen Daukar Doka A Hannu A Najeriya
    Jun 30 2025

    Send us a text

    Kisa ta hanyar daukar doka a hannu na kara ta’azzara da saka damuwa a zukatan ‘yan Najeriya.


    Yayin da wasu ke ganin daukar doka a hannu daidai ne, wasu kuwa na ganin hakan zai cigaba da haifar da rashin doka da oda a kasa.

    Shin ko me doka ta ce a kan daukar doka a hannu da wasu ‘yan Najeriya su’ke yi?



    Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan hanyoyin da za a bi don kawo karshen daukar doka a hannu a Najeriya.

    Show More Show Less
    29 mins
  • Ko Wadanne Dalilai Ne Ke Hana Mata A Arewa Koyon Ilimin Kimiyya?
    Jun 27 2025

    Send us a text

    Doctor Zainab Muhammad na daya daga cikin mata a Arewacin Najeriya da ta jajirce tare da kudirin cika burinta na karantar kimiyya duk da kalubalen da wasu matan dake yankin Arewa suke bayyanawa suna fuskanta wurin karantar fannin.


    Doctor Zainab ba kimiyya kawai ta karanta ba, ta karanci daya daga cikin kimiyyoyin da ake ganin sun fi kowanne wahala wanda a mafi yawan lokuta ba mata kadai ba har da mazan ma na kauracewa wannan karatun.
    Zainab Kwararriyar likita ce wacce ta shahara wurin kula da marasa lafiya a asibitoci.


    Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai duba ne kan dalilan da suka sa matan Arewacin Najeriya ke tsoron karantar ilimin kimiyya.

    Show More Show Less
    30 mins