Najeriya a Yau cover art

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau

By: Muslim Muhammad Yusuf Ummu Salmah Ibrahim
Listen for free

About this listen

Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.

© 2025 Najeriya a Yau
Political Science Politics & Government
Episodes
  • Halin Kunci Da Matan Da Aka Yi Garkuwa Da Su Ke Tsintar Kansu A Ciki
    Nov 20 2025

    Send us a text

    Mata da dama da aka yi garkuwa da su na shiga wani irin mawuyacin hali yayin da suke hannun wadanda suka sace su, suna fuskantar rayuwar kaskanci, da cin zarafi, da muzgunawa da wasu irin yanayi wanda sai ka tausaya musu.


    Irin wadannan mata a wasu lokutan basa tsira da rayukansu, a wasu lokutan kuma ko sun tsira, sukan shiga halin ciwon damuwa wanda ke daidaita musu rayuwa, a wasu lokutan ma har sai sun ji kamar su dauki rayuwar su.


    Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba ne kan irin halin da irin wadannan mata ke shiga da kuma hanyoyin da zasu bi don dawo da martaba a rayuwarsu.

    Show More Show Less
    19 mins
  • Matsayar Doka Kan Taron Da Jam'iyyar PDP Ta Gudanar
    Nov 17 2025

    Send us a text

    Matsayar doka ta zama babbar abun tattaunawa a Najeriya yayin da jam’iyyar PDP ta gudanar da taron ta na kasa duk da mabanbantan hukunce hukunce daga kotuna biyu.


    Umarnin kotu guda yana goyon bayan taron, ɗayan kuwa ya haramta shi gaba ɗaya. Wadannan hukunce hukunce ba baiwa jam’iyyar damar yi ko haramta musu taron kadai suka yi ba, harda baiwa hukumar zabe ta kasa umurnin saka ido ko haramta musu wannan dama yayin taron.

    Duk da wadannan hukunce hukunce, jam’iyyar ta gudanar da taron inda ta zabi shugabannin da zasu cigaba da jan ragamar al’amuranta da kuma daukar wasu kwararan matakai.


    Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

    Show More Show Less
    25 mins
  • Dalilan Da Ke Hana Manoman Najeriya Noman Rani
    Nov 14 2025

    Send us a text

    A duk shekara bayan girbin damina, ana sa ran manoma su ci gaba da noma a lokacin rani domin tabbatar da wadatar abinci da bunkasar tattalin arziki. Sai dai hakan na fuskantar kalubale da dama da ke hana yawancin manoma shiga noman rani.


    Kamar yadda masana suka sha bayyanawa, akwai dalilai da dama dake hana manoma shiga noman rani a duk lokacin da aka ce damina ta tattara inata intat.

    Shin ko wadanne kalubale ne ke hana manoma shiga noman rani bayan damuna ta wuce?


    Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

    Show More Show Less
    27 mins
No reviews yet
In the spirit of reconciliation, Audible acknowledges the Traditional Custodians of country throughout Australia and their connections to land, sea and community. We pay our respect to their elders past and present and extend that respect to all Aboriginal and Torres Strait Islander peoples today.