Najeriya a Yau cover art

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau

By: Muslim Muhammad Yusuf Ummu Salmah Ibrahim
Listen for free

About this listen

Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.

© 2026 Najeriya a Yau
Political Science Politics & Government
Episodes
  • Lokacin Da Ya Kamata A Fara Yakin Neman Zaben 2027
    Jan 8 2026

    Send us a text

    A siyasar Najeriya, akwai ka’idoji da dokoki da ke tsara yadda ake gudanar da zaɓe, ciki har da lokacin da doka ta amince a fara yaƙin neman zaɓe. Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, wato INEC, ita ce ke da alhakin bayyana jadawalin zaɓe da kuma ranar da ‘yan takara za su fara neman goyon bayan al’umma a hukumance.


    Sai dai duk da waɗannan tanade-tanade, ana ci gaba da ganin alamu da ayyuka da ke nuna cewa wasu ‘yan takara suna fara yaƙin neman zaɓe tun kafin a buga gangar siyasa.
    Wannan lamari na bayyana ta hanyoyi daban-daban, kama daga yawan tallace-tallace a kafafen yaɗa labarai, shirya taruka a ɓoye, rabon kayayyaki da kiran jama’a da sunan “taron godiya” ko “ganawar al’umma.


    Shirin Najeriya a yau na wannan lokaci zai yi duba ne kan lokacin da ya kamata ace an fara gangamin yakin neman zabe.

    Show More Show Less
    10 mins
  • Yaya Matsayar Katsalandar Din Da APC Tace Nyesom Wike Na Yi A Jam’iyyar?
    Jan 7 2026

    Send us a text

    A cikin ‘yan kwanakin nan, siyasar Najeriya ta sake daukar sabon salo, bayan barkewar takaddama tsakanin Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, da manyan shugabannin jam’iyyar (APC). Jam’iyyar APC na kallon yadda Wike — wanda ba cikakken ɗan jam’iyyar ba ne amma ke rike da mukami a karkashin gwamnatinta — ke yin katsalandan a harkokin jam’iyyar, musamman a matakin jihohi, a matsayin barazana ga tsarin jam’iyya da ikonta na cikin gida.


    Wannan lamari ya haifar da muhawara mai zafi a tsakanin ‘yan siyasa da masu sharhi kan harkokin siyasa.

    Ko wanne matsaya jam’iyyar APC suka dauka kan wannan batu na katsalandan da Nyesom Wike ke yi a jam’iyyarsu?


    Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

    Show More Show Less
    15 mins
  • Yadda ‘Yan Bindiga Suka Yanka ‘Yan Kasuwa A Jihar Neja
    Jan 6 2026

    Send us a text

    Harin da wasu ‘yan ta’adda suka kai kasuwar Daji da ke karamar hukumar Borgu a Jihar Neja ya sake jawo hankalin al’umma kan matsalar rashin tsaro da ke kara ta’azzara a yankunan karkara na Arewa ta Tsakiya. Kasuwar Daji, wadda ke zama cibiyar hada-hadar kasuwanci ga manoma, ‘yan kasuwa da mazauna kauyuka makwabta, ta kasance wuri na zaman lafiya kafin wannan mummunan lamari da ya girgiza mazauna yankin.


    Batutuwa da dama daga kafafen yada labarai da dama sun bayyana mabanbantan ra’ayoyi kan batun.

    Ko menene hakikanin abun da ya faru a wannan hari da ‘yan bindiga suka kai a kasuwar Daji?


    Wannan shine batun da shirin Najeriya a yau na wannan lokaci zai yi duba akai.

    Show More Show Less
    15 mins
No reviews yet
In the spirit of reconciliation, Audible acknowledges the Traditional Custodians of country throughout Australia and their connections to land, sea and community. We pay our respect to their elders past and present and extend that respect to all Aboriginal and Torres Strait Islander peoples today.