Lokacin Da Ya Kamata A Fara Yakin Neman Zaben 2027
Failed to add items
Add to basket failed.
Add to Wish List failed.
Remove from Wish List failed.
Follow podcast failed
Unfollow podcast failed
-
Narrated by:
-
By:
About this listen
Send us a text
A siyasar Najeriya, akwai ka’idoji da dokoki da ke tsara yadda ake gudanar da zaɓe, ciki har da lokacin da doka ta amince a fara yaƙin neman zaɓe. Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, wato INEC, ita ce ke da alhakin bayyana jadawalin zaɓe da kuma ranar da ‘yan takara za su fara neman goyon bayan al’umma a hukumance.
Sai dai duk da waɗannan tanade-tanade, ana ci gaba da ganin alamu da ayyuka da ke nuna cewa wasu ‘yan takara suna fara yaƙin neman zaɓe tun kafin a buga gangar siyasa.
Wannan lamari na bayyana ta hanyoyi daban-daban, kama daga yawan tallace-tallace a kafafen yaɗa labarai, shirya taruka a ɓoye, rabon kayayyaki da kiran jama’a da sunan “taron godiya” ko “ganawar al’umma.
Shirin Najeriya a yau na wannan lokaci zai yi duba ne kan lokacin da ya kamata ace an fara gangamin yakin neman zabe.